Daga Ahmad Ibrahim Gusau
A wani sabon hari, ‘yan bindiga sun kashe mutane 21 a ƙauyen Bunkasau da ke yankin Zarummai a Ƙaramar Hukumar Bukkuyum ta Jihar Zamfara.
An ruwaito cewa ‘yan bindigar sun mamaye ƙauyen Bunkasau a babura tare da harbe-harbe kan mazauna yankin.
Maharan sun kuma yi garkuwa da mutane da dama, galibinsu mata da yara, tare da kwashe dabbobi a yankin.
Wani mazaunin yankin ya shaida wa wakilinmu cewa maharan sun isa ƙauyen ne a daren Juma’a dauke da makamai na zamani.
“Abin takaici ne, da safe ranar Asabar muka tashi muka ga mutane da yawa an kashe su. Akalla mutane 21 aka kashe, kuma har yanzu muna neman wasu da ba a gano ba; sun gudu daga gidajensu sakamakon harin.”
A cewarsa, an yi jana’izar mutane 21, inda aka binne su a kabari guda a wata al’umma makwabta.
“Don Allah, cikin kuka muna roƙon hukumomi, musamman na jiha da na tarayya, su turo ƙarin jami’an tsaro a yankinmu.”
Da aka tuntubi jami’in hulɗa da jama’a na rundunar ‘yan sandan jihar Zamfara, DSP Yazid Abubakar, ya tabbatar da faruwar lamarin, yana mai cewa har yanzu ba a tantance adadin waɗanda aka kashe ba.
Ya ƙara da cewa rundunar ta tura ƙarin jami’ai domin shawo kan lamarin, kuma an dawo da zaman lafiya a yankin.
