Daga Mahmud Gambo Sani
A kokarin tabbatar da cikakken tsaro, sahin wayar da kai na hukumar kashe gobara ta jihar Kano, karkashin jagorancin Darakta Alhaji Sani Anas, na sanar da al’umma cewa, hukumar ta shirya tsaf tare da daukar dukkan matakan da suka dace domin bayar da kariya ga rayuka da dukiyoyi daga ibtila’in gobara da sauran hadura.
A sanarwar da mai magana da yawun hukumar Saminu Yusif Abdullahi ya sanya wa hannu, sanarwar ta ce, hukumar na jan hankalin masu sayar da iskar gas da gidajen man fetur da masu kantuna da filazozi da kamfanoni da kananan masana’antu da asibitoci da makarantu masu zaman kansu da kuma sauran al’umma da su gaggauta zuwa su yi rijista ko su sabunta rigistarsu a hukumar domin tabbatar da ƙa’idojin tsaro da kuma samun agajin gaggawa.
Hukumar ta bayyana cewa, rashin bin wannan umarni na iya jawo asarar rayuka ko dukiya.
Hukumar na ci gaba da jajircewa wajen wayar da kai da kuma kare al’umma baki ɗaya.
Trending
- Governor Yusuf appoints Emir of Gaya as 2026 Amirul Hajj
- KNSG denies abandoning Murtala Muhammed Library, faults contractor
- ACF suspends BoT chairman over alleged N1.4bn fund diversion
- Nigerian Army kills terrorist, recovers weapons in Kogi
- Appointing Garo as deputy is wisdom for Kano — Danbatta
- Kano strength bilateral ties with UK
- Katsina inaugurates committee for proposed light rail project
- Normalcy returns to Ugep, Idomi after communal clash
